[3/31, 5:39 PM] -Roshni: 20/03/2017
BAKIN GANGA
BY
Mamu
&
Sanam
<<<<<4>>>>>>
Bayan ta gama aikin duk da take, sannan ta samu tayi wanka tayi sallolinta, tana zaune kan sallaya da tayi sallah ne taji sallamar Abbanta, tayi sauri ta tashi ta fito, don ta gaida shi.
“Abba sannu da zuwa”
Ya amsa da
“Yawwa Hamida yar albarka, ince dai komai k’alau?”
Tace
“Lafiya k’alau Abba ”
Yace
“To madallah Hamida Allah ya taimaka.”
Ta tashi ta koma d’akinsu.
*
Hanyar komawa garinsu ya kama, tafiya yake da gudun tsiya, kamar baya son rayuwarshi, sauri kawai yake yaga ya isa Sokoto, ga duhu ya sauka, yasan yanzu hankalin Mamie a tashe yake, ganin har yanzu bai k’arasa ba, ga kuma wayoyin shi duk ba charge a mace suke.
Koda ya iso gida kusan 10 na dare, side d’inshi ya fara shiga yayi wanka, sannan ya shiga cikin gidan.
Mamie na ganin shi ta sauke wani irin ajiyar zuciya,
“Ina ka tsaya har dare yayi haka Hudu?”
Yana k’arasawa wurinta yayi hugging d’inta, yana murmushi. yace
“Ina wuni Mamie?
Ta ansa mishi da
“Lafiya k’alau ya hanya?
Yace
“Hanya kalau Mamiena”
Chuchu dake zaune gefe ta gaida shi ya ansa, Mamie tasa aka kawo mishi abinci ya dan ci kad’an, ya tashi yayi musu saida safe ya wuce side dinshi.
*
Alhaji Jafar asalin d’an Sokoto ne, wanda yake zaune da iyalinsa matarshi Hajiya Maryam, itama haifaffiyar yar Sokoto ce da yaransu 3 Namiji (Hudu) da ‘yan Mata 2, Rukayya (Ummi) sai k’aramar Balkisu (chuchu) da yake Ummi tayi aure shekara 2 da suka wuce, sai ya rage chuchu kawai ke gidan.
Familynsu is a renowned family a garin sokoto, Alhaji Jafar ba k’aramin mai kuddi bane, he’s into harakar gine-ginen gidaje yana saidawa, wasu kuma yasa haya, ba abinda iyalinsa suka nema ya kasa musu.
*
Hudu miskilin mutum ne na k’arshen zance, dalilin haka nema yasa kannensa ba wanda suka shak’u dashi, ko wannensu nesa-nesa yake yi dashi, shidai yaje aiki ya dawo yaga Mamienshi kawai ne aikinsa.
Bayan dawowar shi side d’insa, d’akinshi ya bud’e ya fad’a kan gadon ya kwanta, ya rufe ido don ya samu ya d’an huta, saboda gajiyar da ya kwaso, kwantawar da yayi memories suka fara dawo mishi na yarinyar da ya watsawa ruwa dazun, sai yanzun yake jin ba dad’i, don kuwa yasan inda wata ce d’an neman rashin mutuncin da zata tafka mishi ba k’arami bane, nan take duk yaji rayuwarshi ta b’aci, yayi daya sanin yin hakan, though yasan bawai da gagan yayi mata hakan ba, amma hak’urin da bai bata bane yasa yake jin ba dadi.
(Mrs)
&
Sanam
[3/31, 5:39 PM] -Roshni: [18/3/2017]
BAKIN GANGA
By
Mamu
&
Sanam
****
NOTE: Masu karatu, zaku ga buk ya canja, ya kuma na mutum biyu, dafatar zaku cigaba da binmu.
****
<<<3>>>
Misalin k’arfe shida na Yamma (6:00pm) Tafe take sanye da uniform na islamiya, da jaka ta rataya a kafad’a mai dogon Hannu, a natse take takonta, ta nufi hanyar gidansu. Da ka ganta kai kasan daga Islamiya ta fito.
Tafiya take sauri-sauri kar dare yayi mata a hanya, ga magrib na gabatowa, kawai ji tayi ruwa ya watso mata a jiki, dubawar da zata yi, taga ruwan da suka kwanta a kasan bakin titin layin su ne, wata mota ta fallatso mata a jiki.
Ta d’aga kai ta kalli motar da ta watso mata ruwan, taga wanda yake cikin motar ya samu wuri yayi parking amma bai fito ba, yayi zaman sa yana shan AC abin shi, bin motar tayi da kallo na d’an lokaci, sannan ta ci gaba da tafiyar da take, ta nufi hanyar gidan su bata ce k’ala ba.
Shi kuma ganin hakan da tayi yasa mamaki ya cika shi.
Shigar ta gidan keda wuya Mama Larai ta hau salati
“La’ilaha illallahu ni luba yau me zan gani? Hamida yau kuma wasan k’asa kika koma kina yi tsofai-tsofai da girman ki? Kaicho Hamida wallahi Uwarki dai bata yi sa’ar haihuwa ba Hamida.”
Hamida da tunda mama Larai ta fara magana siraran hawaye ke ta zarya a kumatunta, dama tasan abinda zata tarar kenan.
‘Hamida cikakkiyar budurwa wacce bata wuce shekara 23 da haihuwa ba, yar asalin garin gusau ce (zamfara) mahaifiyar ta ta rasu tun tana da shekaru 3 a duniya, bayan rasuwar mahaifiyarta ne, mahaifinta Mal Sale ya k’ara aure inda ya aure Larai yar mak’otansu, wadda tun mahaifiyar Hamida tana raye suke mutunci da ita sosai asali ma la’akari da hakan da Mal Saleh yayi ne yasa ya aurota, domin ta zamo uwa a gun Hamida.
Sai dai inaa! Larai ta zamo masa k’adangaren bakin tulu, yana gani take musgunawa Hamidar shi daya fi so fiye da komai a rayuwa, amma ba yanda zaiyi.
Mal saleh Family, zamu iya ce muku they are from a middle class family (Ma’ana su ba masu kuddi ba suba talakawa ba).
Dai-dai gwargwadon hali yana kwatanta masu. Hamida tana da kanne biyu, domin kuwa Mama Larai ta haifi yara biyu bayan auren su, mace da namiji, Rahma da Imam.
“Mama wallahi ina tafiya ne wani mai mota ya watsa min ruwan dake kwance bakin titi”
Hamida ta amsata fuska cike da hawaye.
“To Hamida gani yayi kin masa kama da bola, ba dole ya watsa miki ruwan ba, yo miye marabar ki da bolar ne, ai ni wallahi yamin dai-dai, don wallahi da zan ganshi koda bani da abinda zan bashi zan masa godiya, had’e da saka mishi albarka, tsinanniyar banza kawai, ni ki wuce zuwa d’ora min abinci kinji ko, azaluma shine ki kai zaman ki wurin yawon iskancin ki don kar muci abinci ko? To wallahi idan zaki kai isha’i baki dawo ba ki sani sai kin dawo kin d’ora shi.” Inna Larai ta idar da fad’anta tana huci, ita a dole an b’ata mata rai.
Da taga duk bai mata ba, Ta dauko butar da ke gefenta ta jefe Hamida da ita.
(Mrs)
&
Sanam
[3/31, 5:39 PM] -Roshni: 20/03/2017
BAKIN GANGA
By
Maryam Alkali (Mamu)
&
Nafisa Aliyu Musa (Sanam)
<<<<6>>>>
Ya tashi ya wuce side dinshi ranar ko dinner bai yi ba, yayi salloli ya zauna ya d’auko laptop d’inshi, ya fara aiki har wuraren 11 na dare, baiyi bacci ba.
Duk bayan mintina takan fad’o mishi a rai, yayi deciding gobe ma ya koma ko zai ganta ya nemi gafararta, da tunani bacci ya dauke shi.
Safiya ta waye as usual yaje ya gaida su Dady ya wuce office, 12 nayi ya kama hanyar gusau, yau ma kamar jiya haka yayi ta wahalar nema, amma inaa! bai samu wanda ya gane ko bayanin da yake ba, ballantana ya samu wanda ya santa.
Wuraren 4pm ya kama hanyar dawowa sokoto, a haka sai da ya jera 2 weeks yana zuwa nemanta amma ba nasara, mutanen unguwar har sun kular mishi, ya d’an fara sabawa dasu, bama kamar Mal Bala mai faci, da yake idan Hudu yaje yakan dan yi musu Ihsani.
Tun baya damuwa har abun ya fara damunshi, wani sa’in ma gani yake kamar ba mutum bace, yana tunanin k’ila Aljana ce, don ko idan ba haka nan ba ya za’ayi ya watsa mata ruwan d’auda (datti) har a fuska kuma bata ce mishi komai ba, ta kama hanya tayi tafiyarta, sannan kuma unguwar da abin ya faru yazo yafi sau 12 amma ace ba wanda ya santa.
*
‘Zaune ya sameta akan wani dutsi ta had’a kai da gwiwa tana ta rusa kuka, irin kukan nan mai sosa zuciya, ganinta a wannan wurin cikin wannan yanayi ya k’ara d’aga mishi hankali.
“Subhanallahi baiwar Allah me kike yi nan ke kad’ai zaune? kuma kina ta rusa kuka haka?”
Sam bata d’ago kai ta kalli mai maganarba, sai dai ta d’an tsagaita kukan da take.
“Ya salam! don girman Allah kiyi hak’uri ki daina kukan nan da kike yi, ta d’ago kai sama ta kalle shi, suna hada ido yaji gabanshi yayi mummunar fad’uwa, ganin cewa yarinyar da yake ta faman nema ce.
Nan take ya zube akan gwuiwoyinshi ya had’a hannunshi biyu sama, yace “Don girman Allah ki yafemin, Nine wanda na watsa miki ruwa da mota, tun ranar na kasa sukuni, don Allah ki yafe min.”
Hamida da tunda ya fara magana ta tsura mishi ido tana kallonshi, ya cigaba da cewa “Don Allah ki yafe lmin ko zan samu natsuwa……….”
Kiran sallar masallacin gidansu ya tad’a shi, daga mafarkin da yakeyi, yai firgigit ya tashi yana salati, ya zauna yasa hannuwanshi ya rufe fuska yana mamakin abinda ya faru.
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un na shiga ukku, yanzu har mafarkin yarinyar nan na farayi” ya zauna yayi shiru na d’an mintuna sannan ya tashi yayi alwala, ya wuce masallaci.
Chan ya samu Dady, sukayi sallah suka d’auki Al-qur’ani suka fara karatu har sai da haske ya fito, sannan suka shiga gida.
Daddy ya wuce cikin gida, Hudu kuma ya wuce side dinshi.
Da yake yau Saturday ba aiki, ya nema wuri kawai ya kwanta yana tunano mafarkin da yayi yau.
By
(Mrs)
&
Sanam
[3/31, 5:39 PM] -Roshni: 20/03/2017
BAKIN GANGA
By
Mamu
&
Sanam
<<<<5>>>>
Da tunanin abun kwana (Bacci) ya dauke shi, safiya ta waye ya shirya yaje yin sallama da Mamie, koda yaje Dady ma yana zaune a parlour tare da Mamie, nan ya gaidasu ya tashi ya wuce office.
*
Hamida kuwa bayan ta idar da sallar asuba ta shiga aikace-aikacen gida, saida ta tsaftace gidan kaf sannan ta d’ora musu zazafen (d’umame) tuwo, ta dama kunu tayi duk abinda tasan ya kamata tayi, sannan ta shiga tayi wanka ta koma d’aki tana jiran masu gidan su tashi, da yake ta gama secondary school kuma Mama Larai ta hana a saka ta jami’a wai aure ya kamata ayi mata, ita bazata iya zama tana had’a kafada da ita ba, shiko Abba yace bazai mata auren dole ba sai ranar da ta kawo wanda take so sannan zaiyi mata aure.
*
Hudu kam sunan yana office d’inne kawai, amma ga baki d’aya hankalinshi ba’a wurin yake ba, don kuwa har yanzu tunanin yarinyar jiya yake yi.
Anya kuwa wannan yarinyar mutum ce? Meyasa batayi mishi rashin mutunci akan abinda ya mata ba? Meyasa ko magana ma baiga tayi mishi ba? Meyasa ta k’yaleshi tayi tafiyar ta?
Bayan yana tuna yanda ruwan ya zuba har a fukarta ya kuma b’ata duk kayan dake jikinta, abubuwan dake ta yi masa yawo akai kenan, nan take yaji yana son zuwa Gusau ko Allah zai had’ashi da ita, ya samu ya bata hakuri, ko zai samu sukuni a zuciyarshi.
Nan take ya tashi ya kwashi makullan motarsa, ya kama hanyar garin gusau.
Tafiyar Awa biyu da ‘yan mintina ta kaishi garin gasau.
Da shigarshi bai tsaya ko’ina ba sai dai-dai wurin da ya watsa mata ruwan jiya, yana tsayawa ya hau tambayar mutane, kowa yace mishi bai gane wadda yake magana ba.
Yayi ta tambayar mutane amma bai samu wanda ya gane ta ba, a haka har wuraren 5:30 ganin dare na k’arasowa gashi har yanzu bai samu wanda ma ya gane yarinyar ba, yasa ya kama hanya ya komawar shi sokoto.
7:40pm dai-dai ya iso gida, wurin Dady ya fara zuwa ya gaidashi, sannan ya wuce d’akin Mamie koda yaje ya same ta zaune akan sallaya, ya gaida ita.
“Hudu ina ka shiga ne yau kayi dare? Ko duk aikin ne yayi yawa?”
“No wallahi Mamie gusau naje.”
“Gusau kuma? Ta fad’i cike da mamaki”
Nan take ya kwashe duk abinda ya faru ya fad’a mata, tayi shiru ta jinjina abin sannan tace
“Gaskiya baka kyauta ba, amma ba wani abin da zaka tada hankalinka bane, da har zaka kama hanya kaje har gusau neman gafararta, gashi kuma kaje ka k’ona mai da lokacinka a banza, baka samu ganin Yarinyar ba.”
Yace
“Mamie bazaki gane bane wallahi yarinyar was looking so innocent, Allah ina office sai tunanin abin nike, ni gabaki d’aya ya hanani sukuni, Mamie ya zanyi?
Ya k’arashe maganar yana langwab’ar da kai, Uwa wani jinjiri.
“Hudu ka kwanatar da hankalinka, na fad’a maka ba wani abin tada hankali bane, watak’ila ma yarinyar ta yafe maka, shiya saka bata ce maka komai ba ta wuce abinta.”
By
(Mrs)
&
Sanam
[3/31, 5:39 PM] -Roshni: [3/26, 2:59 PM] ~Roshni~: [Sunday, March 26, 2017]
BAKIN GANGA
BY
MAMU
&
SANAM
<<<7>>>
***
Haka Hudu ya wuni jiki a Mace, yana tunano ‘Yar Zamfarawa, duk motsin da yayi tana lik’e a ransa.
Wani irin Abu yake ji yana fiskarshi zuwa gareta, kamar wani magic, baya da kwanciyar hankali idan bai ganta ba, musamman wannan mafarkin da yayi da ita.
Gashi Mamynshi ta kasa ta tsare, ta hana shi fita, a cewarta sai ya huta a weekend d’innan, ko b’angarensa hanashi fitowa tayi, komai na buk’ata aika masa ake yi.
Hudu bai tab’a ganin Monday tayi masa nisan zuwa ba, irin wannan.
Ya k’agara ya fita ofis yaje Gusau, ko mafarkinsa zai zama gaskiya.
“Haba Hudu ruwa kawai ka watsa mata fa, amma ka dame kanka, sai kace kad’eta kayi ta karye.”
Zuciyarshi tayi masa wannan tuni, amma shi kam ya kasa gane meke faruwa dashi.
*
Misalin k’arfe 7:15am na safiyar Litinin (Monday), sai ga Hudu shar cikin shirinsa na fita ofis. Yayi b’angaren iyayensa ya gaidasu.
Mamy sai mamaki takeyi, “sammakon meye haka na fita zuwa ofis hudu?”
Tayi mashi wannan tambayar tana ajiye carbin hannunta.
“Wanda ke fita har after 9 yau shine before 8 ma zai fita.” yace mata “Wani aiki mai muhimmanci zaiyi a ofis yau.”
Addu’ar kariya tayi masa, ya fice, ko break ya kasa tsayawa.
*
Fitarshi daga Unguwarsu, hanyar barin gari ya d’auka, ko ofis baya jin zaya iya zuwa, sai yaje ya tabbatar da mafarkin da yayi.
Tafiya kusan ta Sa’a d’aya (1hour) yayi, gaf da zai shiga Mafara sai ga kira daga ofis, cewar maza-maza yazo ana nemansa.
Ba yadda ya iya dole ya juya mota, ya dawo hanyar sokoto, yana ta tsaki, kwata-kwata an b’ata masa lissafi.
Gudu yake ta shararawa, yazo sokoto yayi abinda zaiyi a ofis, ya juya Gusau.
*
“Hamida! Hamida!! Hamida!!!”
Iman ce keta bud’ar bakin kiran Hamida, tazo tayi mata wankin kayan islamiyarta.
Yarinyar tayi bala’in raina Hamida saboda irin cin mutuncin da taga mahaifiyarta nayi mata, bata la’akarin da fin shekarun da Hamida ta bata.
Wanka Hamida takeyi, ai da sauri ta juye ruwan a jikinta, ta d’auro zani ta fito, tana karkarwar sanyi.
“Lafiya kike k’wala min kira haka Imani?”
Cikin sanyin murya tayi mata wannan tambayar, tana tsane jikinta da k’aramin zane.
Uniform d’inta ta watso mata a jiki, sai warin zufa (gumi) sukeyi, Hamida tayi saurin d’auke numfashinta. Imani tace
“Maza ki wanke min, idan sun bushe ki hura charcoal iron (dutsen garwashi) ki goge min, bana son kuma rashin hankali, don kika k’ona min kaya irin yadda kika yi kwanan baya zaki ga me zan maki a gidan nan.”
Inna Larai dake cikin d’aki ta fito, tana tambayar lafiya Imani ke d’aga murya, itada waye?
“Nida wannan jakar mana Inna, nayi mugun tsanarta.”
Wata dariya Inna ta kice da ita, “kiyi min maganinta kawai Imani, nima ba son bud’e ido nake na ganta ba, amma anyi kwantai sai lokacin sadaka ya sauka.”
Tuni Hawaye sun fara yiwa Hamida ambaliya a fuska, har kirjinta take jin yana mata zafi, ta rasa me ta tsarewa wad’annan bayin Allah.
Kwasar kayan tayi ta fara wankewa, tana tsartar da yawo, saboda Imani irin matan nan ne masu warin k’ashi.
*
Hudu kam gudun da yake shararawa na yayi sauri ya dawo sokoto har ya b’aci, ya take mota son ransa, kamar baya gudun faruwar wani Abu…..
[3/31, 5:39 PM] -Roshni: [3/31, 3:30 PM] -Roshni:
BAKIN GANGA
By
Mamu
&
Sanam
<<<8>>>
***
Gudu sosai Hudu yake shararawa, bai auni ba, sai jin yayi karo da wata mota mai zuwa .
Mai motar yayi over taking din wata mota, shi duk a tunaninsa Hudu ya ganshi, zai sauka a titi, ya bar masa wuri ya wuce, don har wuta ya matsa masa.
Bai San Hudu hankalinsa yana sokoto ba, sai kaura da juna kawai suka ji sunyi.
Dukansu Basu k’ara sanin inda Kansu yake ba, sai jama’a masu wucewa ne sukayi parking domin yin taimako, bayan motocinsu sun dame da juna.
Da k’yar aka zaro kowannesu, sunyi jina-jina da jini, aka kwashesu aka k’arasu dasu sokoto, a asibitin U.D.U.T.H tare da taimakon ‘yan sanda na kusa.
*
Accident & Emergency akayi dasu da gaggawa. Likitoci suka fara duba su.
Bayan awa biyu, likitoci suka gama duba su, kowannensu an masa dressing duk inda suka ji ciwo, tare da allurori.
*
Daga nan fa aka fara Neman ‘yan Uwansu, wancan d’ayan kam an samu ‘yan uwansa dake mafara, ta hanyar wayarsa dake jikinsa, sun kamo hanya suna ta kuka.
Matarsa Basira tana fad’in “Yanzun nan ya baro gida, har muna rikicin akan ba zanje bikin suna ba, na tsaya nayi masa tuwo kafin ya dawo, ni kuma na kafe sai naje ko bai barni fa.”
Ta fyace majina, tana kiran “Kar ka mutu Ashafa, na fasa zuwa bikin, kuma zanyi maka tuwon.”
A hanyar zuwansu ne, sun kawo wurin da had’arin ya faru ne, suka ga yadda motocin suka yi, kai kace ba za’a samesu da rai ba.
Sosai suka k’ara rud’ewa, tare da b’arkewa da sabon kuka.
Basira sai fad’i take “Na zama Bazawara Ni Basira.”
Kakarsa ce ta kwab’e bakinta, tana ta sababi.
*
Hudu kam duka wayoyinsa rufe suke GAM da password, an rasa ya za’ayi a neme ‘yan uwansa, sai kashe wayoyin wata nurse take tana k’ara kunnawa, amma wayoyin sai nuna a saka password suke.
Haka aka hak’ura har zuwa Yamma, babu abinyi, har hukumar asibitin tace za’a je a bada sanarwa, sai ga Mamy tayi kiransa, taji ko lafiya yake yau, ta jishi shiru.
Da karkawa Nurse ta d’aga wayar, ganin sunan Mamy rubuce a screen din wayarsa d’aya.
“Hello! Good Evening Ma’am.”
Nurse ta fad’a da sauri.
Tuni cikin Mamy ya kad’a, jin Mace ta d’auki wayar d’anta.
“What is Happening to my Son pls? And Who are you?”
Mamy ta fad’a kamar ta fashe da kuka.”
“Ma’am, Rush to the Hospital (U.D.U.T.H) now, your Son…..”
Ai Mamy bata Bari ta k’arasa bayanin ba, ta tsinke wayar, a guje ta dauko mayafi, ta fice a gidan ita da direba.
A hanya take kiran Daddy su had’e a asibitin.
Tana shiga asibiti ta k’ara kiran wayar, Nurse d’in ce tayi mata kwatance har d’akin da yake, sai da ta iso k’ofar d’akin sannan ta katse kiran.
Kuka sosai Mamy takeyi, ganin halin da hudu da yake ciki, ga drip an d’aura masa, ga bandage a hannu da k’afa.
Baccinsa yake yi bai san a ina yake ba.
A lokacin Daddy ya k’araso, Mamy ta fad’a jikinsa tana kuka, bata damu da jama’a dake wurin suna kallonsu ba, fad’i take “Pls ka gaya masa kada ya mutu ya barni. I can’t do with out Him.”
Har da had’awa da dukan kirjin Daddy.
Ganin jama’ar dake wurin hankalinsu ya dawo garesu, yasa Kunya ta rufe Daddy, ya jata zuwa cikin d’akin, yana lallashi.
Had’e da tambayarta “Ya abin ya faru?”
Hawayenta ta goge, tace “Nima ban sani ba.”
Nurse din dake wurin ce tayi masu bayanin yadda abin ya faru, daga hanyar Mafara aka zo dasu, sunyi accident.
Ido suka zaro, sanin su dai ba suyi da hudu ba, cewar zai je Gusau yau ba.
Ya saba duk zai je aikinsa na ofis, sai ya kirasu a waya sunyi masa Allah ya tsare hanya.
Ba abinda ya fad’owa Mamy a rai, sai yarinyar da hudu yake damuwa da ita kwanan nan, wacce ya watsawa ruwa.
“‘Yar Zamfarawa”
Mamy ta furta a fili, ta juyu tana kallon Daddy sosai.
“Aikam idan har zuwa wurinta ne Hudu ya had’u da wannan masifar, ba shakka Yarinyar ‘Yar Mayu ce, sai nasa an d’aureta daga ita har iyayenta.”